Gobara ta kona gidan jigon Darikar Tijjaniyya, Sheik Mansur Kaduna

Shugaban Majalisar Malamai Na kugiyar Fityanul Islam Ta kasa Reshen Babban Birnin Tarayya Abuja, Imam Murabbi Cisse Alyarwawy Ya Shiga Jerin Sahun ‘Yan Uwansa Jagororin Tarikar Tijjaniyya Da Suka Jajantawa Dan Uwansu Shahararran Malamin nan Na Tariqar Tijjaniyya Sheikh Mansur Kaduna Bisa Jarrabawar Gobara Da Allah Ya yi masa Jiya Da Daddare Misalin karfe 2:00 Na Dare A Gidansa Dake Unguwar Kabala a jihar Kaduna.

Na kira Wayarsa Yau Misalin karfe 9:00 Na Safe Don In Jajantamasa Bayan Na Sami Labarin Abinda Ya Faru Wacce Ta Sabbaba Masa Asarar Dukiya Da Littattafa Masu Yawan Gaske.

Sai Ya Daga Wayata Yana Mai kelkelewa Da Dariya Yana Mai Cewa “Shehu Murabbi Ka ji Abinda Mai Kaya Ya yi Da Kayansa Ko” Sai Ya Dawo Shine Mai Jaje Maimakon Shi Za A Jajantawa.

Take Wannan Dariya Tasa Yayin Ibtila’i Ta Tunatar Da Ni wani Hadithin Sayyidina Abdullahi Bn Umara R.T.A Wanda Imamun Nawawy Ya Kawo Shi Cikin Littafinsa (Al Azkaru).

Ga Hadithin Kamar Haka “Abdullahi Bn Umara Ya Binne Wani Dansa Sai Ya kelqele Da Dariya Sai Aka Ce masa Shin Za ka yi Dariya Wajen kabari Sai Yace Ina So ne n Tirmuza Hancin Shaidan”

Tabbas Na san Ba Komai Bane Ya Janyo Wa Dan Uwa Sheikh Ibrahim Mansur Imam Kaduna Wannan jarrabawar Illa Kusancin sa Ga Allah Da Cikar Kamalar Ma’rifarsa.

Allah Ka Bashi Ikon Cin Wannan Jarrabawa, Ka Azurta shi Da Ninke Niken Abinda Ya Rasa Albarkar Maulana Rasulullahi Sallallahu Alaihi Wa A’lihi Wasallama. Wama Zalika Allallahi Bi Aziz.

More News

Mutane uku sun mutu a ruftawar wani ginin bene a Kano

Hukumar Bada Agajin Gaggawa Ta Ƙasa NEMA ta tabbatar da mutuwar mutane uku bayan da wani bene mai hawa uku ya ruguzo a unguwar...

Ganduje Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Shirya Zanga-Zangar Neman A Sauke Shi

Shugaban jam'iyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ce gwamnatin jihar Kano ta jam'iyar NNPP ita ce ke da alhakin shirya zanga-zanga iri...

Qatar za ta taimaki marayu a Najeriya

Gwamnatin kasar Qatar ta bayyana cewa za ta ba da tallafi ga yara marayu sama da 1,000 da suka rasa iyayensu saboda rikicin Boko...

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...