Dalilin da ya sa muka rufe iyakar Najeriya da Benin – Buhari

Shugaban kasa Muhammad Buhari ya ce Najeriya ta rufe kan iyakarta da Benin ta mashigar Seme dake Lagos domin dakile ayyukan masu fasa kaurin shinkafa.

Kwanaki takwas kenan da mashigar take a rufe kuma wasu rahotanni sun bayyana cewa mashigar ta Seme za ta shafe tsawon kwanaki 28 a rufe.

Da yake magana lokacin da yake ganawa da Patrice Talon takwararsa na jamhuriyar Benin a wurin taron cigaban ƙasashen Nahiyar Afirka da ake yi a birnin Yokohama na kasar Japan. Buhari ya ce fasa kwaurin na kawo barazana ga tsare-tsarensa a fannin noma.

A cewar Femi Adesina mai magana da yawun shugaban kasar, Talon ya ce rufe iyakar ya jefa mutanen jamhuriyar Benin cikin mawuyacin hali.

A cewar shugaban kasar rufe kan iyakar zai bawa jami’an tsaro damar fitar da wani tsari da zai kawo karshen matsalar baki daya.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...