Boko Haram Ta Yi Garkuwa Da Mutane 14 a Garin Kwalfata | VOA News

Lamarin dai ya faru ne a wasu jerin hare-hare da mayakan Boko Haram ke kaiwa jihar Arewa Mai Nisa dake kasar Kamaru, inda a garin Kwalfata suka kama mutane 14 da suka hada da maza da mata, wadanda ya zuwa wannan lokaci babu wanda ya san inda suke.

Da yake yiwa Muryar Amurka karin bayani kan hare-haren, mazaunin yankin Alhaji Yaya Barista, ya ce karancin jami’an tsaro da sakaci a yankin sune ke haddasa karuwar hare-haren da ‘yan Boko Haram ke kaiwa.

Boko Haram dai na amfani da jiragen kwale-kwale a yankin biyo bayan toshe wasu hanyoyi da ruwa ya yi, lamarin da ya haifarwa jami’an tsaro tsaiko ga shiga yankunan domin bayar da kariya ga al’ummar.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ÆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...