BBC Hausa: Gobara ta ƙona kimanin shaguna 50 a kasuwar Singa

Yadda gobara ta ƙona shaguna a kasuwar Singa

Wata gobara ta tashi a kasuwar Singer ranar Lintinin, ta haifar da asara mai ɗinbin yawa.

Rahotanni sun ce wutar ta ƙona dukiya wadda har yanzu ba a iya tantancewa ba.

Wannan dai shi ne karo na hudu da ake samun gobara a baya-bayan nan a kasuwanni daban-daban na jihar Kano.

Bayanai na cewa gobarar ta auku ne da tsakar dare sanadiyar fashewar wani babban abin sanyaya ruwa a layin Savannah cikin babbar kasuwar ta Singer.

Wani mutum da lamarin ya auku a kan idonsa ya ce wutar ta yi mummunar barna.

“Duk wani da ke da rumfa a cikin inda gobarar ta faru bai iya fitar da komai ba,” in ji shi.

Alhaji Dan Azumi, wanda shi ne wakili a gidan Savannah, wurin da aka yi wanann gobara ya ce asarar da gobarar ta haddasa ta miliyoyin nairori ce.

Ya ce “za a samu store kamar 50; akwai wanda yake da taliya, akwai kuma wanda yake da suga da kuma na kayan sinadarin miya.”

Ya ƙara da cewa akwai wanda ya sauke kayan sanadarin miya tirela biyar kwana ɗaya kafin ranar da gobarar ta tashi.

Alhaji Dan Azumi ya ce a yanzu suna da kiyasin an yi asarar “biliyan biyu da wani abu.”

Ƙarin labarai:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano ta tattabar da aukuwar gobarar.

Jami’in hulda da jama’a na hukumar, Saminu Yusuf Abdullahi ya ce wutar ta samo asali ne daga ɗakin sanyaya ruwa, sannan ya yaɗu zuwa wasu kantunan.

Ya ƙara da cewa rashin kyakkyawan tsarin ajiye kaya a kasuwar ya taimaka wajen iza wutar.

Sai dai ya ce ba a samu rahoton rasa rai ko kuma na jikkatar wani ba a sanadiyyar gobarar.

Wannan dai ita ce gobara ta uku cikin kasa da wata biyu da ta auku a kasuwanni daban-daban a jihar Kano.

Kasuwar Singer dai babbar kasuwa ce da ake hada-hadar kayan masarufi daga sassan Najeriya har ma da ketare.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...