Ahmed Buhari wani yaro ne mai shekara 17 wanda ya ke da baiwar lissafin da kuma saurin girka.
A cewar mahaifiyarsa an haife shi ne yana da bukata ta musamman, dan haka yake fama da hardewar harshe.
Samun wannan labari ya sa BBC ta je Lafiya jihar Nassarawa, domin ganin irin baiwar lissafi da Allah ya yi masa.
Da kuma irin saurin da ke gare shi da kwatankwacin irin saurin da ya ke yi wurin amsa tambaya daya ko kuma fiye da haka.