Ana Kokawa A Kan Fyade Da Ake Yiwa ‘Yan Gudun Hijira A Njeriya

Wani rahoto da aka fitar a baya yace kungiyar Human Rights Watch ta nuna bacin ranta na rashin yin abin da ya dace wajen kare irin wadannan matan da tabbatar da ‘yancinsu da kuma tabbatar da sun samun ababen more rayuwar.

Kungiyar ta tattara bayanan a kan lalata da kuma yiwa ‘yan mata 43 fyade, wadanda suke zaune a sansanonin gudun hijira guda bakwai dake Maiduguri a jihar Borno.

An samu irin wannan labari a wani sansanin ‘yan gudun hijira dake jihar Adamawa, inda aka yiwa wata ‘yar gudun hijira dake da tabun hankali fyade, wanda yanzu haka ta samu juna biyu, lamarin da yasa kungiyoyin fafutuka ke cewa dole a gudanar da bincike.

Kwamared Abubakar Abdul Salam dake zama shugaban kungiyar Progressive Mind For Development Initiative, PMDI, yace akwai bukatar a sa ido a kan abubuwan dake faruwa a sansanonin ‘yan gudun hijira a Najeriya.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]