An sanar da zaman makoki na kwana biyar saboda mutuwar shugaban kasa a Iran

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya sanar da zaman makoki na kwanaki biyar saboda rasuwar shugaban kasar Ibrahim Raisi wanda ya mutu a hatsarin jirgin sama mai saukar ungulu.

Wani jirgin sama mai saukar ungulu dauke da Raisi ya gamu da abin da ministan harkokin cikin gida Ahmad Vahidi ya tabbatar da cewa “sauka ne mai wuya” a ranar Lahadi.

Kamfanin dillancin labaran Iran ya labarto cewa, tashar talabijin ta Press TV ta Iran ta bayar da rahoton cewa, lamarin ya afku ne a kusa da birnin Jolfa mai tazarar kilomita 600 daga arewa maso yammacin Tehran babban birnin kasar ta Iran.

Rahotanni sun ce jirage masu saukar ungulu uku na cikin ayarin, yayin da sauran biyun suka koma ba tare da wata matsala ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan YaÆ™i Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin Æ™wazon jagorancinsa wajen yaÆ™i da ta’addanci da magance matsalar tsaro a Æ™asar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiÆ™a da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]