An Kaddamar Da Sabon Sansanin Sojan Najeriya A Birnin Gwari | VOA Hausa

Babban Hafsan Hafsoshin Rundunar sojojin saman Najeriya Air Marshall Sadique Baba Abubakar ya ce, sun kuma tura jiragen yakin nan da Najeriya ta sayo daga kasar Italiya don wannan aiki.

Babban Hafsan sojojin saman Najeriyar ya ce, sun kuma tura karin bataliyar mayakan sama na musamman wato “special forces” da za su yi aiki daga kasa, duk dai a kokarin cimma yan ta’addan.

Sadique Abubakar ya ce sojojin saman Najeriya za su yi ta yakar ‘yan bindigar har sai sun tabbatar da tsaro a yankin na Birnin Gwari da ma sauran shiyyar Arewa Maso Yamma.

A cewar mai sharhi kan sha’anin tsaro Mohammed I. Usman, irin wannan hobbasar lalle ka iya ‘yin tasiri sosai wajen kawo karshen ‘yan bindigar.

More News

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

ĆŠan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...

Musulmi a Zaria sun yi taron addu’o’i saboda mummunan halin matsi da Najeriya ke ciki

Musulmi a garin Zaria na jihar Kaduna, sun gudanar da addu'a ta musamman domin neman taimakon Allah kan halin da 'yan Najeriya ke ciki...