Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya zo da iska mai karfi mai gudun tsiya ne ya yi sanadin wannan rashe rahen rayuka da asarar dukiyoyi a garin Mutum Biyu. Hakazalika wasu da dama kuma sun samu raunuka.
Wani mutum mai suna Muhammad Sanusi Gambo, wanda ya shaidi al’amarin kuma ya na cikin wadanda su ka je makabarta yin jana’izar mamatan, ya ce a gaban idonsa aka bisne yara bakwai wadanda akasari gine gine ne su ka fada kansu. Ya ce guda bakwai din wadanda ma ya sani Kenan, banda wadanda su ka mutu a sassan garin. Ya ce gidaje dai dai ne a bayan gari da bas u rushe ba.
Mallam Hashim Musa, daya daga cikin iyayen da su ka rasa ‘ya’yansu sakamakon ambaliyar, ya ce bayan da ya ji kukan yaransa sai ya je ya yi ta kwaye bulo bulo ya samu daya dansa da rai ya zakulo shi; bayan da ya sake komawa, sai ya tarar da dayarsa ta mutu cikin baraguzan bulo, ya zakulo gawarta. Shi ma Alhaji Khalil Umar, daya daga cikin iyayen da su ka rasa ‘ya’yansu ya ce gini ne ya fadi kan dansa. Duk wani kokarin jin ta bakin Shugaban Karamar Hukumar ya ci tura.