Ambaliyar Ruwa Ta Halaka Yara 7, Ta Rusa Gidaje Sama Da 200

Al’ummar Karamar Hukumar Gassol da ke jahar Taraba ta arewacin Najeriya na cikin matukar tashin hankali biyo bayan wata mummunar ambaliya wadda ta yi sanadin salwantar rayukan yara a kalla bakwai baya ga rushewar gidaje sama da dari biyu. Tuni wasu da dama da su ka rasa muhallansu su ka nemi mafaka a ginin makarantun gwamnati.

Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ya zo da iska mai karfi mai gudun tsiya ne ya yi sanadin wannan rashe rahen rayuka da asarar dukiyoyi a garin Mutum Biyu. Hakazalika wasu da dama kuma sun samu raunuka.

Wani mutum mai suna Muhammad Sanusi Gambo, wanda ya shaidi al’amarin kuma ya na cikin wadanda su ka je makabarta yin jana’izar mamatan, ya ce a gaban idonsa aka bisne yara bakwai wadanda akasari gine gine ne su ka fada kansu. Ya ce guda bakwai din wadanda ma ya sani Kenan, banda wadanda su ka mutu a sassan garin. Ya ce gidaje dai dai ne a bayan gari da bas u rushe ba.

Mallam Hashim Musa, daya daga cikin iyayen da su ka rasa ‘ya’yansu sakamakon ambaliyar, ya ce bayan da ya ji kukan yaransa sai ya je ya yi ta kwaye bulo bulo ya samu daya dansa da rai ya zakulo shi; bayan da ya sake komawa, sai ya tarar da dayarsa ta mutu cikin baraguzan bulo, ya zakulo gawarta. Shi ma Alhaji Khalil Umar, daya daga cikin iyayen da su ka rasa ‘ya’yansu ya ce gini ne ya fadi kan dansa. Duk wani kokarin jin ta bakin Shugaban Karamar Hukumar ya ci tura.

More News

An kashe kwamandan soji a Katsina

An kashe kwamandan sojoji na wani sansanin soji da ke Sabon Garin Dan’Ali a karamar hukumar Danmusa a jihar Katsina a wani harin kwantan...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...