Dalilin da yasa aka tura da karin ‘yan sanda jihar Borno

Yan sanda zasu taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya a yankin arewa maso gabashin Najeriya

Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta ce za ta tura da karin ‘yan sandan kwantar da tarzoma dubu biyu da kuma kwararun jami’anta kan yaki da ta’addanci tare da karnuka masu iya sansano abubuwa zuwa yankin arewa maso gabashin kasar.

Ta ce ‘yan sanda za su taimaka wa sojoji a yakin da suke yi da ‘yan kungiyar Boko Haram.

A wata sanarwa da kakakin ‘yan sandan na Najeriya Jimoh Moshood ya fitar a ranar Lahadi, ya ce umarnin hakan wanda Supeto Janar na rundunar ya bayar, yana daga cikin tanadin aikin ‘yan sanda domin tabbatar da zaman lafiya da bin doka da oda.

Mai ba babban supeton ‘yan sanda shawara kan hulda da manema labarai Bala Ibrahim ya ce ssojoji na samun galaba a yakin da suke yi da Boko Haram kuma ‘yan sanda za su je ne domin su taimaka mu su.

“Ba wai ‘yan sanda ne zasu je gaba ba,’yan sandan za su je wurare ne da sojoji suka murkushe ‘yan Boko Haram domin su tabbatar da zaman lafiya da doka da oda a wadannan wurare” in ji shi

Hukumomin Najeriyar dai na daukar wannan mataki ne a yaki da ‘yan Boko Haram a wannan lokaci da masu ikirarin Jihadin ake ganin suna tsananta hare-hare a kan sojojin kasar a yanzu.

More from this stream

Recomended