Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark.
Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa.
Mai shari’a Musa Liman ya ce Abejide bai gabatar da gamsassun hujjojin da suka nuna an take masa haƙƙi ba sakamakon sauyin shugabancin da aka samu a jam’iyyar.
Alƙalin ya kuma tabbatar da cewa sauyin shugabanci daga tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu, zuwa David Mark bai saɓa wa kundin tsarin mulkin ADC ba.
Haka kuma, kotun ta umarci Abejide ya biya kowanne daga cikin waɗanda ake ƙara Naira miliyan 2, yayin da lauyansa zai biya Naira miliyan 10 a matsayin kuɗaɗen shari’a.
Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

