An Gurfanar Da Mutum 24 Kan Kisan Wata Mata A Kaduna



Rundunar ’yan sandan jihar Kaduna ta gurfanar da mutum ashirin da huɗu a gaban kotu bisa zargin hannu a kisan wata mata da aka zarga da satar yaro a yankin Maraban Jos.

Kakakin rundunar, Mansir Hassan, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Lamarin ya faru ne ranar Lahadi bayan wasu fusatattun mutane sun kai hari kan matar bisa zargin cewa ta saci wani yaro, duk da cewa babu hujjar da ta tabbatar da zargin.

A cewar Hassan, jami’an ’yan sanda sun samu kiran gaggawa, inda jami’in kula da yankin ya jagoranci tawagar jami’ai zuwa wurin domin ceto matar tare da kai ta ofishin ’yan sanda domin kariya da bincike.

Sai dai ya ce daga baya wasu mutane sun mamaye ofishin ’yan sandan, suka rinjayi jami’an da ke bakin aiki sannan suka kwace matar kafin su kashe ta tare da kona gawarta.

’Yan sandan sun ce ana tuhumar waɗanda ake zargin da laifuffuka da suka haɗa da haɗa baki domin aikata laifi, tayar da tarzoma, lalata kadarorin gwamnati da na ’yan sanda da kuma kisan kai.

Kotun ta ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar ashirin da ɗaya ga watan Yuli, yayin da aka tsare waɗanda ake zargin a gidan gyaran hali.

A nasa martanin, Kwamishinan Yaɗa Labarai na jihar Kaduna, Ahmed Maiyaki, ya yaba wa rundunar ’yan sandan jihar kan matakin gaggawar gurfanar da waɗanda ake zargi.

Ya ce, “Governor Uba Sani’s administration will not tolerate any form of mob action or jungle justice. We urge residents to always report suspected criminal activities to security agencies and allow the law to take its course.”

Ya ƙara da cewa duk wanda aka samu yana ɗaukar doka a hannu zai fuskanci hukunci ba tare da la’akari da matsayinsa ba.

More from this stream

Recomended