NAHCON ta  kammala aikin kwaso alhazan Najeriya daga Saudiya

Hukumar Aikin Hajji ta Najeriya, NAHCON  ta sanar da kammala aikin dawo da alhazan Najeriya gida bayan da aka kammala aikin hajjin shekarar 2026.

Wata sanarwa da hukumar ta fitar ta ce jirgin karshe da ya ɗauko alhazan jihar Zamfara zai iso Najeriya a ranar Talata 23 ga watan Yuni abin da ya kawo karshen aikin dawo da alhazan gida.

A cewar sanarwar alhazan Najeriya 12 ne dake dauke da ciwo iri ri daban-daban ke kwance a asibiti inda suke samun kulawar likitoci a ƙasar ta Saudiyya.

Hukumar ta ce tana bibiyar halin da su ke ciki sau da kafa kuma ta kammala shirin yadda za su dawo gida Najeriya da zarar sun samu sauki an sallame su daga asibiti.

Shugaban hukumar ta NAHCON Ismail Yusuf  ya nuna godiyarsa kan yadda aka kammala aikin hajjin na bana cikin nasara.

Yusuf ya kuma ya bawa shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu da mataimakinsa Kashim Shettima kan goyon bayan da suka bayar wajen wajen samun nasarar aikin hajjin na bana.

More from this stream

Recomended