
Jumullar yan Najeriya 115 masu tafiya cirani aka dawo da su gida bayan da suka makale a jamhuriyar Nijar.
Yan ciranin sun sauka ne a filin jirgin saman Mallam Aminu Kano da tsakar ranar Talata.
Nura Abdullahi jami’in gudanarwa a hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Kasa NEMA shi ne ya tabbatarwa da jaridar The Cable labarin.
A cewar wasu rahotanni an kwaso mutanen ne daga birnin Agadez na jamhuriyar Nijar bisa wani yanayi dake da rudarwa.
Amma kuma Abdullahi ya musalta rahoton inda ya ce an kwaso mutanen ne bisa radin kansu da taimakon hukumar dake lura da yan Gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya IOM da kuma taimakon hukumar dake lura da yan gudun hijira a Najeriya da kuma hukumomin gwamnati da dama.
Ya ƙara da cewa kasar Nijar ce take da wani sansani na hukumar ta IOM da ake ajiye yan Afrika wadanda suka yi kokarin tafiya cirani kasashen Turai amma suka makale.
Ya ce IOM tana haÉ—a kai da kasashen Afrika wajen taimakawa a kwashe yan kashe su da su ka makale a mayar da su gida.

