Sojoji sun ceto mata da yara  360 da aka ɗauke daga garin Ngoshe dake Borno

Rundunar sojan Najeriya ta ce dakarunta na rundunar Operation Haɗin Kai dake aikin samar da tsaro a yankin arewa maso gabas  tare da haɗin gwiwar dakarun tsaron na musamman sun samu nasarar ceto mutane 360 yawancinsu mata da ƙananan yara da ƴan ta’adda suka yi garkuwa da su daga Ngoshe a karamar hukumar Gwoza ta jihar Borno.

Manjo janar Abdulsalam Abubakar kwamandan rundunar tsaro ta haɗin gwiwa a yankin arewa maso gabas ya fadawa kamfanin Dillancin Labaran Najeriya cewa an samu nasarar ceto mutanen a wani tsararren farmaki da aka kai a wurare da dama dake kusa da tsaunukan Mandara.

A cewarsa zaratan dakaru na musamman ne suka fara kai farmakin farko abun da ya rikita yan ta’addan hakan ne kuma ya bawa dakarun sojan Birged na 26 samun damar kuɓutar da mutanen.

“fararen hular da aka kuɓutar na daga cikin mazauna garin Ngoshe da aka yi garkuwa da su a ranar 3 ga watan Maris a harin da yan bindiga su ka kai garin,” ya ce.

Ya kara da cewa aikin ceto yazo da yar matsala bayan da ƙananan yara biyu suka mutu saboda wahalar sarkakiya da wuyar da yankin yake da shi idan ana tafiya.

Duk mutanen da aka ceto an yi musu gwaje-gwaje lafiya inda aka garzaya da waɗanda suke cikin mawuyacin hali ya zuwa asibitin garin Gwoza.

More from this stream

Recomended