Dikko Radda Ya Ce Tinubu Zai Lashe Zaben 2027



Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya bayyana kwarin gwiwar cewa Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu zai sake lashe zaben shugaban kasa na shekarar 2027.

Radda ya bayyana hakan ne bayan kada kuri’arsa a zaben fidda gwani na jam’iyyar APC, inda ya ce yadda mutane suka fito kwansu da kwarkwatarsu ya nuna karfin goyon bayan da jam’iyyar ke da shi a jihar.

Ya ce tururuwar fitowar jama’a a lokacin zaben na nuni da yadda ‘yan jam’iyya ke da kwarin gwiwa kan APC da kuma tsarin dimokuradiyyar cikin gida.

Gwamnan ya kuma ce yadda aka gudanar da zaben cikin lumana ya nuna fahimtar siyasa da dattako daga al’ummar Katsina.

A cewarsa, jam’iyyar APC za ta ci gaba da tabbatar da adalci da bai wa dukkan ‘yan jam’iyya dama iri daya wajen shiga harkokin siyasa da zabuka.

More from this stream

Recomended