Jam’iyyar APC ta sanar da ɗage zaɓen fidda gwani na gwamna a jihohin Bauchi da Kwara zuwa ranar Juma’a, 22 ga watan Mayu, 2026.
Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da kwamitin gudanarwa na ƙasa na jam’iyyar ya fitar ranar Alhamis.
Jam’iyyar ta kuma tsawaita zaɓen fidda gwani na kujerun majalisar dokokin jihar Zamfara na mazaɓun Maradun ta ɗaya da Maradun ta biyu zuwa ranar Lahadi, 24 ga watan Mayu.
APC ta ce an amince da sauyin jadawalin ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da gudanar da zaɓe cikin gaskiya, lumana da tsari.
Jam’iyyar ta bayyana cewa sauyin ya shafi zaɓen gwamna a Bauchi da Kwara da kuma kujerun majalisar dokokin jihar Zamfara kawai.
APC Ta Ɗage Zaɓen Fidda Gwani A Bauchi Da Kwara

