Tinubu Ya Naɗa Matashi a Matsayin Sabon Shugaban JAMB

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya naɗa Farfesa Segun Aina a matsayin sabon shugaban hukumar shirya jarabawar shiga jami’a ta JAMB.

Aina mai shekaru talatin da tara zai maye gurbin Farfesa Is-haq Oloyede, wanda wa’adinsa zai ƙare a ranar talatin da ɗaya ga watan Yulin shekarar dubu biyu da ashirin da shida.

A cikin wata sanarwa da kakakin shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar, Tinubu ya bayyana sabon shugaban a matsayin ƙwararren masani mai gogewa a harkokin jarrabawa, fasahar intanet da sauye-sauyen al’umma.

More from this stream

Recomended