Tsawa Ta Kqshe Sufeton ‘Yan Sanda a Borno



Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta tabbatar da mutuwar wani sufeton ‘yan sanda mai suna Abdulkadir Garba, wanda aka fi sani da “Buratai”, bayan tsawa ta buge shi yayin da yake bakin aiki a Maiduguri.

Kakakin rundunar, ASP Nahum Daso, ya ce lamarin ya faru ne ranar Laraba yayin da mamacin da wani babban jami’i, ASP Wazani Adamu, suka yi ƙoƙarin neman mafaka kafin fara ruwan sama.

Ya bayyana cewa tsawar ta bugi jami’an biyu kafin su isa inda za su fake, amma ASP Wazani Adamu ya tsira da ransa.

Daso ya ce marigayin ya rasu ne sakamakon ƙonewar da ya samu a jikinsa bayan bugun tsawar.

Rundunar ta bayyana marigayin a matsayin jami’i mai jajircewa wajen gudanar da aikinsa da kuma tabbatar da zaman lafiya duk da tsananin yanayi.

More from this stream

Recomended