
Babbar kotun tarayya dake Kaduna ta bawa tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai izinin zuwa asibiti a duba lafiyarsa musamman ido da kuma hakori a wasu asibitoci dake Abuja.
J.Okor Odey Shugaban sashen hulda da yan jaridu na hukumar ICPC dake yaki da masu yiwa tattalin arzikin ƙasa zagon ƙasa ne ya bayyana cewa kotun ta amince da bukatar ne a ranar Laraba.
Odey ya ce lauyan dake kare El-Rufai ya nemi kotu da ta umarci hukumar ta bawa El-Rufai damar ganin likitoci domin su duba lafiyarsa.
Ya ce kotun ta bada umarni da akai El-Rufai duk wani asibiti da yake so ciki har da asibitin hakori na Mike Dental Clinic da asibitin ido na Eye-Q dukkan su dake Abuja.
“Kotun ta jaddada cewa dukkanin zirga-zirgar zuwa asibitin ta kasance karkashin kulawar ICPC,’ a cewar Odey.
A ranar 24 ga watan Maris ne hukumar ICPC ta gurfanar da El-Rufai da Joel Adoga a gaban kotun inda ta je zargin su da aikata zamba da kuma almundahanar kuɗaɗe.

