Gwamnatin Jihar Kogi ta bayyana cewa an samu nasarar ceto yara 15 daga cikin wadanda aka sace a wata makaranta da gidan marayu da ke Zariagi.
Kwamishinan yada labarai na jihar, Kingsley Fanwo, ne ya bayyana hakan a ranar Litinin a Lokoja, inda ya ce maharan sun sace yara 23 tare da matar mai makarantar a daren ranar 26 ga Afrilu.
Ya ce jami’an tsaro karkashin jagorancin ‘yan sanda tare da hadin gwiwar sauran hukumomi sun kai dauki cikin gaggawa, wanda ya kai ga ceto yawancin yaran.
Fanwo ya kara da cewa ana ci gaba da kokarin kubutar da sauran wadanda suka rage a hannun masu garkuwa da mutane.
Gwamnatin ta nuna damuwa kan yadda ake gudanar da wasu makarantu da gidajen marayu ba tare da rajista ba, musamman a wurare masu nisa, tana mai cewa hakan na iya jefa yara cikin hadari.
Ta kuma bukaci masu irin wadannan cibiyoyi da su bi dokokin gwamnati tare da tuntubar hukumomi domin tabbatar da tsaro.
Gwamnatin ta jaddada kudurinta na kare rayuka da dukiyoyin al’umma tare da ci gaba da ayyukan tsaro har sai an shawo kan lamarin gaba daya.
Gwamnatin Kogi Ta Ce Ta Ceto Yara 15 Daga Cikin Wadanda Aka Sace A Gidan Marayu

