Jam’iyar NDC na zawarcin Obi da Kwankwaso

Jam’iyar National Democratic Party, NDC  ta roki Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso da Peter Obi da su shiga jam’iyar su yi takara a zaɓen shekarar 2027.

A wani sako da ta wallafa a ranar Lahadi NDC ta haskawa manyan ƴan siyasar cewa kwanaki 14 ne  su ka rage musu domin shiga jam’iyar su yi takara.

Sakon da jam’iyar ta wallafa ya bayana cewa yanzu makonni biyu ne kaɗai ya rage kafin wa’adin mika sunayen ƴan jam’iyya ya cika.

Sakon na dauke da hoton  Obi da Kwankwaso suna gaisawa inda aka rubuta cewa Najeriya za ta yi garau da harshen turanci.

A makon da ya gabata ne magoya bayan Kwankwaso da Obi su ka kafa wata kungiya da ake kira OK Movement domin neman goyon bayan jama’a ga takarar Obi da Kwankwaso.

Har yanzu jam’iyar ADC da jiga-jigan ƴan siyasar su ke ciki tana fama da rikici abun da ke barazana ga takara a ƙarƙashinta a zaɓen 2027.

More from this stream

Recomended