Rikici tsakanin Isra’ila da ƙungiyar Hezbollah ya sake ƙamari, inda ɓangarorin biyu ke zargin juna da karya yarjejeniyar tsagaita wuta da aka tsawaita kwanan nan.
Rundunar sojin Isra’ila (IDF) ta sanar da cewa ta kai hare-hare kan motocin harba rokoki na Hezbollah guda uku a kudancin Lebanon cikin dare. A cewar IDF, motocin na ɗauke da makamai kuma suna zama barazana ga sojojinta da fararen hular Isra’ila. Ta kuma jaddada cewa za ta ci gaba da ɗaukar matakai domin kawar da irin waɗannan barazanar.
A nata ɓangaren, Hezbollah ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar da safiyar yau cewa ita ma ta kai hari kan sojojin Isra’ila.
Wannan na faruwa ne bayan tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin ɓangarorin biyu na tsawon mako uku, kamar yadda shugaban Amurka ya sanar a baya-bayan nan.
Sai dai duk da hakan, kowanne ɓangare na ci gaba da zargin ɗayan da take yarjejeniyar, lamarin da ke nuna ƙara tsananta rikicin a yankin.
Isra’ila Da Hezbollah Sun Ci Gaba Da Musayar Wuta

