Tinubu Ya Rantsar Da Sabon Ministan Gidaje



Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya rantsar da Dr. Muttaqha Rabe Darma a matsayin sabon ministan gidaje na Najeriya.

Dr. Darma, ɗan asalin jihar Katsina, ya maye gurbin Ahmed Musa Dangiwa, wanda ya yi murabus a kwanakin baya.

An gudanar da bikin rantsarwar ne a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, inda manyan jami’an gwamnati suka halarta.

A yayin bikin, Shugaba Tinubu ya bayyana amincewarsa da ƙwarewar sabon ministan, yana mai cewa yana da tabbacin Dr. Darma zai bayar da gudunmawa wajen bunƙasa ɓangaren gidaje a ƙasar.

More from this stream

Recomended