Kungiyar agaji ta Médecins Sans Frontières (MSF) ta bayyana damuwa kan yadda matsalar jin ƙai ke ƙara tsananta a yankin arewa maso gabashin Najeriya.
Kungiyar ta ce hare-haren baya-bayan nan da ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai suka kai a jihar Borno sun raba sama da mutum 500,000 da muhallansu.
A cewarta, iyalan da suka tsere zuwa garin Pulka da ke kusa da iyakar Kamaru na fuskantar mawuyacin hali, inda suke rayuwa a sansanonin da suka cika maƙil, tare da ƙarancin abinci, ruwa da kuma tsafta.
Rahoton ya ƙara da cewa mayaƙan Boko Haram da wani ɓangaren ƙungiyar da ya balle sun ƙara tsananta hare-hare a watannin baya-bayan nan, inda suke kai farmaki kan dakarun tsaro da fararen hula a yankin.
MSF Ta Yi Gargaɗi Kan Ƙara Tsanantar Matsalar Jin Ƙai A Arewa Maso Gabas

