Peter Obi Ya Nemi Ƙawance Da Arewacin Najeriya Gabanin Zaɓe



Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya jagoranci wata babbar tawaga ta ƴan siyasar kudu maso gabas domin ƙulla ƙawance da arewa maso gabas da sauran yankunan ƙasar nan.

Obi ya bayyana haka ne ranar Alhamis a Bauchi bayan wata ganawa ta sirri da ya yi da gwamnan jihar, Bala Muhammad, tare da masu ruwa da tsaki kan batun haɗin gwiwar siyasa.

Ya ce manufar wannan yunƙuri ita ce haɗa kan ‘yan ƙasa domin ciyar da Najeriya gaba, musamman yayin da ake tunkarar zaɓe mai zuwa.

Rahotanni sun nuna cewa Obi na ci gaba da zagayawa sassa daban-daban na ƙasar domin tattaunawa da shugabanni da ‘yan siyasa kan yiwuwar ƙawance.

A makon da ya gabata kuma, magoya bayan Peter Obi da na Rabi’u Musa Kwankwaso sun kafa wata ƙungiya mai suna “OK Movement”, wadda ke fafutukar ganin an goyi bayan takarar Obi da Kwankwaso a matsayin shugaban ƙasa da mataimaki a jam’iyyar ADC.

More from this stream

Recomended