Tinubu ya rantsar da Darma a matsayin ministan gidaje

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a ranar Juma’a ya rantsar da Engr Muntaka Rabe Darma a matsayin sabon ministan gidaje da bunkasa birane.

Da yake magana da yan jaridar fadar shugaban kasa bayan ya karbi rantsuwar kama aiki Darma ya bayyana cewa yasan irin girman aikin dake gabansa inda ya ci alwashin kammala shi.

“Inaji a jikina cewa an ɗora mini wani nauyi kuma nasan cewa idan an ɗora maka nauyi akwai rukunin mutane uku za su auna irin ƙoƙarinka,” ya ce.

“Ina so na gamsar da kai na cewa aikin da aka bani ina yinsa yadda ya kamata. Daganan mutanen da suke tare da ni za su gamsu sannan sauran al’umma baki ɗaya suma za su gamsu. A ƙarshe Allah ne zai zamo mini sheda.”

Darma ya ci alwashin cewa nan bada jimawa ba kadan al’umma za su ga canji.

Loading

Signing-in 3 seconds...

Signing-up 3 seconds...