
Ƴan ta’adda a ranar Alhamis sun kai farmaki kan sansanin sojoji dake Benisheikh a jihar Borno inda su ka kashe dakarun soja.
A wata sanarwa ranar Alhamis Michael Onoja daraktan yaɗa labarai a ma’aikatar tsaro ya ce yan ta’addan sun kai harin ne da misalin ƙarfe 12:30 na daren ranar Alhamis.
Ya ce dakarun soja ƙarƙashin jagorancin, Birgediya Janar Oseni Braimah kwamandan birged ta 29 sun mayar da martani cikin juriya tare da nuna kwarewa da yin amfani da manyan bindigogi da su ka fi na yan ta’addar abun da ya tilasta musu janye wa daga farmaki.
Sanarwar ta bayyana takaici na asarar rayukan da aka samu a ɓangaren dakarun.
Onoja ya ce nan gaba kaɗan za a fitar da ƙarin bayani kan dakarun da suka mutu bayan an sanar da iyalansu a hukumance.
Ya yi kira da jama’a da su yi watsi da wasu labarai da wasu kafafen yaɗa labarai ke bayarwa kan harin.yan
Kawo yanzu dai babu wata ƙungiya da ta ɗauki nauyin alhakin kai harin

