Shugaban jam’iyar APC ya bawa wadanda su ka jikkata a rikicin Jos tallafin miliyan 15

Nentawe Yilwatda shugaban jam’iyar APC na kasa ya bayar da tallafin naira miliyan 15 ga mutanen da su ka jikkata a harin da yan bindiga su ka kai Unguwar Rukuba dake ƙaramar hukumar Jos North ta jihar Filato.

Yilwatda ya sanar da bayar da tallafin kuɗin ne a ranar Asabar a yayin ziyarar da ya kai wa waɗanda da suka jikkata da ake samun kulawa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos.

A ranar Lahadin makon da ya gabata ne aka kashe aƙalla mutane 28 a wani hari da wasu yan bindiga su kai unguwa

Shugaban na APC ya ce an bayar da tallafin kuɗin ne domin taimakawa musu wajen biyan kuɗin magani tare da rage musu nauyin dawainiya.

Ya bayyana harin a matsayin dabbanci da baza a yarda da shi inda ya kara da cewa ” dole ne a kawo karshen kashe-kashe a jihar Filato,”

More from this stream

Recomended