Tinubu zai kai ziyarar jaje jihar Filato

Shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya ɗage tafiyar da ya shirya yi zuwa Iperu a jihar Ogun inda ake sa ran zai buɗe filin jirgin saman  Gateway da aka samar a jihar.

A wata sanarwa ranar Laraba, Bayo Onanuga mai magana da yawun shugaban kasar ya ce a maimakon haka Tinubu  zai je Jos babban birnin jihar Filato inda zai jajantawa mutanen da harin ƴan bindiga ya shafa .

Onanuga ya ce dalilin ziyarar shi ne jajantawa gwamnatin jihar da kuma mutanen da suka rasa yan uwa a harin da kuma a rikicin da ya biyo baya.

Ya kara da cewa daga Jos shugaban kasar zai wuce ya zuwa Lagos inda zai yi hutun Easter.

Ziyarar shugaban kasar na zuwa ne biyo bayan ganawar da ya yi da gwamnan jihar Caleb Mutfwang a fadar Aso Rock a ranar Laraba.

More from this stream

Recomended