Gwamnoni sama da 10 sun halarci taron addu’ar cikar shugaba Tinubu shekaru 74

Gaggan ƴan siyasa na Najeriya da kuma wasu shuwagabannin addinai sun tattaru a babban masallacin ƙasa dake Abuja inda su ka gudanar addu’ar cikar shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu shekaru 74 a duniya.

A cikin waɗanda suka halarci wurin taron addu’ar akwai mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima, mai bawa shugaban kasa shawara kan sha’anin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu yan majalisar kasa da kuma gwamnoni ciki har da na jihar Gombe, Inuwa Yahaya wanda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin jihohin arewa.

Addu’ar ta samu jagorancin fitattun malaman addinin musulunci Sheikh Ibrahim Maƙari da kuma Muhammad Kabir.

A yayin addu’ar malaman sun roki Allah ya yiwa shugaban kasar jagora, ya bashi hikima da juriya ya yin da yake jagorantar kasa a ƙasa musamman a fannin kawo sauye-sauyen  siyasa da tattalin

Malaman sun kuma shawarci shugabanni da su yi mulki da gaskiya da rikon amana.

More from this stream

Recomended