
Hukumar ICPC dake yaki da hana ci da karɓar rashawa ta saki tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai.
Tun ranar 19 ga watan Fabrairu ne ke tsare da El-Rufai.
Jami’an hukumar sun kama shi ne bayan da jami’an hukumar EFCC su ka sake shi inda ya shafe kwanaki a hannunsu ya na amsa tambayoyi.
Sakin nasa na zuwa ne sa’o’i kaɗan bayan rasuwar mahaifiyarsa kasar Masar.
Wani makusancin tsohon gwamnan ya tabbatarwa da jaridar Daily Trust cewa an sake shi sai dai ya gaza ƙarin haske kan batun.
Bashir El-Rufai dan gidan tsohon gwamnan ya tabbatar da cewa an saki mahaifin nasa.
Akwai kwararan alamu karara dake nuni da cewa an sake shi ne bisa tausayawa sakamakon rashin mahaifiyar ta sa da ya yi.

