Wasu ’yanbindiga sun kai hari gidan sakataren ƙaramar hukumar Kibiya da ke jihar Kano, inda suka yi awon gaba da shi a wani farmaki da aka kai da daddare.
Shugaban majalisar kansilolin ƙaramar hukumar, Hon. Sabo Yusuf Usman, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa harin ya auku ne a daren Juma’a a garin Dinya.
A cewarsa, “Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:00 na dare, lokacin da sakataren ke barci a gidansa.”
Ya ƙara da cewa maharan sun fara ne da tayar da ɗan sakataren da ke kwana a zauren waje, inda suka tilasta masa ya ƙwanƙwasa ƙofar gidan. Daga nan sai yaron ya sanar da mahaifinsa cewa cikinsa na ciwo, lamarin da ya sa sakataren ya buɗe ƙofa, ba tare da sanin abin da ke faruwa ba.
Rahotanni sun ce daga nan ne ’yanbindigar suka shiga gidan suka tafi da sakataren zuwa wani wuri da ba a sani ba. Har zuwa yanzu, babu cikakken bayani daga hukumomin tsaro kan lamarin.
Ƴanbindiga Sun Sace Sakataren Karamar Hukumar Kibiya A Kano

