Wani jigon jam’iyar PDP ya tsallake rijiya da baya a jihar Benue

Wasu da ake zargin yan bangar siyasa ne sun kai wa jigon jam’iyar PDP, Cif Bemgba Iortyom farmaki inda su ka cinnawa motarsa wuta a Makurdi babban birnin jihar Benue.

Iortyom wanda ya kasance kwararre dake shawartar jam’iyar PDP kan harkokin sadarwa a jihar Benue ya ce lamarin ya faru a da misalin karfe 08:30 na dare akan titin George Akume dake birnin.

Ya ce wasu mahara ne kusan su biyar dake kan babura biyu suka tare motarsa lokacin da ya ke ƙoƙarin tsayawa inda su ka fara kiran waya.

A cewarsa maharan dake  É—auke da Æ™ananan gatari sun tunkare shi abin da ya tilasta masa fita daga motar ya gudu domin tsira da lafiyarsa. Ya ce daganan sai suka watsawa motar kirar Pugeuot 406 fetur tare da kunna mata wuta.

Ya kara da cewa tuni aka sanar da jami’an yan sanda rahoton faruwar lamarin inda su ke cigaba da gudanar da bincike domin ganowa tare da kama waÉ—anda su ke da hannu a ciki.

More from this stream

Recomended