Gowon ya yi kira ga yan Najeriya su cigaba da hakuri da gwamnatin Tinubu

Tsohon shugaban kasa, Yakubu Gowon  ya ce shugaban kasa , Bola Ahmad Tinubu ya na duba muradun Najeriya ta kowane bangare.

Da yake magana ranar Asabar bayan wata ziyarar da ya kai wa Tinubu a fadar Aso Rock dake Abuja, Gowon ya ce shugaban kasar ya na iya bakin kokarin sa wajen magance matsalolin dake addabar kasar nan.

Ya ce ya ziyarci shugaban kasar ne domin ya gode masa kan irin ƙoƙarin da gwamnatinsa take yi.

” Na zo na ganshi na kuma gode masa kan dukkanin kyawawan ayyukan da ya ke yiwa kasa,” a cewar Gawon lokacin da yake magana da yan jaridu.

“Dole mu yi duba da dukkanin kyawawan ayyukan da shugaban kasa ya ke yi da kuma cigaban da Najeriya ta ke samu ta fannin tattalin arziki da sauransu,” ya ce.

Gowon ya shawarci yan Najeriya da su kasance masu hakuri tare da goyon bayan gwamnati domin samar da zaman lafiya da hadin kan ƙasa.

More from this stream

Recomended