Ƙungiyar Hamas ta Falasɗinawa ta bukaci Iran da ta daina kai hare-hare kan maƙwabtan ƙasashe a yankin Gabas ta Tsakiya.
A cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar, ta jaddada cewa Iran na da ƴancin kare kanta daga hare-haren Isra’ila da Amurka.
Sanarwar ta ce: “Kuna da ƴancin kare kanku ta dukla hanyar da kuke da ita, bida dokokin duniya, amma muna kira ga ƴan’uwanmu na IRan du daina kai hare-hare zuwa makwabtan ƙasashe”.
Hamas ta bayyana cewa kiran nata na nufin rage tashin hankali a yankin, tare da kauce wa faɗaɗar rikicin zuwa sauran ƙasashe.
Tun bayan ɓarkewar rikicin da ya haɗa Isra’ila da Amurka a gefe guda, da Iran a wani ɓangare, Tehran ta riƙa kai hare-hare kan wasu ƙasashen yankin Gabas ta Tsakiya da kuma sansanonin sojin Amurka da ke ƙasashen.
Hamas Ta Bukaci Iran Ta Dakatar Da Hare-Hare Kan Maƙwabtan Ƙasashe

