Trump: Ni Da Netanyahu Za Mu Yanke Shawarar Kawo Karshen Yaƙi Da Iran

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa kawo ƙarshen yaƙin da ake yi da Iran zai buƙaci amincewarsa tare da ta firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu.

Jaridar The Times of Israel ta ruwaito cewa Trump ya faɗi hakan ne yayin wata tattaunawa ta waya da aka yi da shi, inda ya ce shi da Netanyahu sun daɗe suna tattaunawa kan batun. Ya ƙara da cewa “zai yanke shawara a lokacin da ya dace”.

Lokacin da aka tambaye shi ko Isra’ila za ta iya ci gaba da yaƙi da Iran idan Amurka ta dakatar da hare-haren da take kai wa, Trump ya ce: “Ba na ganin hakan zai zama dole.”

Dangane da naɗin Mojtaba Khamenei a matsayin sabon jagoran addinin Iran, Trump ya ƙi yin tsokaci kai tsaye kan batun, yana mai cewa: “Za mu ga abin da zai faru.”

Sai dai a baya Trump ya nuna adawarsa da naɗin Mojtaba, inda ya taɓa cewa: “Ɗan Khamenei ba abin da zan amince da shi ba ne.”

More from this stream

Recomended