China Ta Yi Yunƙurin Sasanta Yaƙin Iran Da Amurka Da Isra’ila

Jakadan gwamnatin China na musamman kan harkokin Gabas ta Tsakiya, Zhai Jun, ya kai ziyara ƙasar Saudiyya a wani yunƙuri na shiga tsakani domin rage tashin hankalin da yaƙin da ake yi tsakanin Iran da Amurka da Isra’ila ya haifar.

Zhai Jun ya bayyana cewa Beijing a shirye take ta yi aiki tare da Saudiyya domin ƙarfafa ƙoƙarin samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin Tekun Fasha.

A yayin ziyarar, jakadan ya gana da Ministan Harkokin Wajen Saudiyya, Yarima Faisal bin Farhan Al Saud, da kuma Babban Sakataren Ƙungiyar Ƙasashen Yankin Gulf (GCC), Jasem al-Budaiwi.

A ganawarsa da Yarima Faisal a ranar Litinin, Zhai ya nuna matuƙar damuwa kan tashin hankalin da ke ƙaruwa a yankin, yana mai jaddada muhimmancin mutunta ikon ƙasashe, tsaronsu da kuma iyakokinsu.

Har ila yau, ya ce ya kamata a yi Allah wadai da duk wani hari da ke jawo asarar rayuka ko lalacewar wuraren fararen hula da wuraren da ba na soja ba.

Jakadan ya kuma sake nanata kiran da China ke yi na a dakatar da duk wani hari na soji nan take domin buɗe ƙofar tattaunawa.

More from this stream

Recomended