Iyalan El-Rufai Sun Soki Ci Gaba Da Tsare Tsohon Gwamnan na Kaduna

Iyalan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun bayyana cewa ci gaba da riƙe shi a tsare ya saba wa dokokin Najeriya, inda suka kuma zargi ana amfani da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa wajen muzgunawa ’yan hamayya.

Iyalan sun bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da Bello El-Rufai ya fitar a madadinsu ranar Juma’a, 6 ga watan Maris.

A cikin sanarwar, Bello El-Rufai ya ce tsare tsohon gwamnan ba bisa ka’ida ba ne, yana mai bayyana matakin a matsayin “saɓa doka.”

Ya kuma yi zargin cewa ana amfani da hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a matsayin wata hanya ta takura wa masu adawa da gwamnati.

Iyalan sun buƙaci a bi doka da oda wajen tafiyar da lamarin, tare da mutunta haƙƙin tsohon gwamnan kamar yadda kundin tsarin mulkin ƙasa ya tanada.

More from this stream

Recomended