Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo ta tabbatar da kama wasu mutane biyu bisa zargin hannu a kisan wata mata mai shekara 62 a birnin Ibadan.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Juma’a.
Rahotanni sun nuna cewa an kashe matar ne a ranar Laraba a yankin Ori Apata da ke karamar hukumar Ido a Ibadan. Lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin mazauna yankin.
A sabuwar sanarwar da rundunar ta fitar, ta ce an kama mutane biyu da ake zargi da hannu a lamarin. An bayyana sunayensu a matsayin Muhammed Sanusi mai shekara 42 da kuma Ogbu James Ajah mai shekara 40. Dukkansu mazauna yankin Ori-Apata ne a karamar hukumar Ido.
Rundunar ta ce bincike na ci gaba, kuma ana kokarin cafke duk wani da ake zargi da alaka da kisan.
Ƴansanda a Najeriya Sun Kama Mutane Biyu Kan K¡san Wata Mata Ƴar Shekara 62

