Atiku ya zargi APC da shirya yiwa ADC zagon ƙasa

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya yi zargin cewa jam’iyar APC mai mulki na shirin yin amfani da ɓangaren shari’a wajen yiwa jam’iyyar ADC zagon ƙasa.

Ya kuma shawarci jagororin ayan adawa da su sanya idanu don ganin shirin bai tabbata ba.

Atiku ya fadi haka ne  ranar Alhamis da daddare a yayin wata ziyara da ya kai gidan tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai.

A ranar Alhamis Muyiwa Adekeye maitaimakawa El-Rufai kan kafofin yada labarai ya yi zargin cewa jami’an tsaro sun yi ƙoƙarin kama tsohon gwamnan a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe dake Abuja bayan da ya dawo daga kasar Masar.

Da yake nasa jawabin Atiku ya ce ya samu sahihan bayanai ka shirin da jam’iyar APC ta ke.

“Kamar yadda su ka yiwa PDP zagon ƙasa akwai kokari da kuma shirin yiwa ADC zagon ƙasa ta sake  yin amfani da ɓangaren shari’a,” a cewar Atiku.

” Dole mu zama ciki shirin kar ta kwana dole kuma mutashi tsaye kan shirin yiwa yan adawa zagon ƙasa,”

Atiku ya kuma yi allawadai da abun da ya bayyana da yinƙurin da aka yi na muzanta El-Rufai.

Ya ce muzanta El-Rufai da aka yi tamkar muzanta yan adawa ne baki daya.

Da yake tofa albarkacin bakinsa El-Rufai ya godewa Atiku kan ziyarar da ya kai masa da kuma  goyon baya da yake bashi.

More from this stream

Recomended