Yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 73 a Zamfara

Akalla mutane 73 ne aka bada rahoton anyi garkuwa da su biyo bayan harin da yan bindiga suka kai ƙauyukan Buzugu da Rayau a karamar hukumar Bukuyyum ta jihar Zamfara.

Zagazola Makama dake wallafa bayanan kan sha’anin tsaro ya bayyana cewa an kai farmakin da karfe 02:45 na daren ranar 18 ga watan Oktoba.

A cewarsa yan bindigar masu yawan gaske ɗauke da muggan makamai sun farma ƙauyukan biyu inda suka yi awon gaba da wasu mazauna ciki ya zuwa wani wuri da ba a a sani ba.

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa ana cigaba da kokarin ganin an kubutar da dukkanin mutanen tare da dawo da zaman lafiya a inda lamarin ya faru.

Har ila yau majiyar ta bayyana cewa jami’an tsaro da kuma yan bijilante dake yankin na cigaba da zafafa bincike a yankin.

Al’ummomi da dama dake jihar Zamfara na cigaba da fuskantar hare-hare daga yan bindiga.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]