Jami’an hukumar NDLEA dake yaƙi da hana sha da kuma fataucin miyagun ƙwayoyi sun tsare wata mata ƴar shekara 35 mai suna, Chidimma Okene.
An tsare matar ne bayan da aka kama ta tana ƙoƙarin safarar ƙunshi 20 na ganyen tabar wiwi mai nauyin 10.70Kg da aka ɓoye cikin abincin ƙabilar Igbo da ake kira Abacha da kuma busassun kayan lambu lokacin da take hanyar zuwa garin Doha dake ƙasar Qatar ta filin jirgin Saman Murtala Muhammad dake Lagos.
Hukumar ta ce jami’anta da haɗin gwiwar jami’an hukumar DSS ne suka samu nasarar kama matar lokacin da ake tantance fasinjojin da suke shirin hawa jirgi.
Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi ya ce Chidimma tana zaune ne a ƙasar Qatar kuma ta dawo gida Najeriya domin yin bikin Kirsimeti.
Chidimma ta ce an ajiye ta ne a Club Dice Hotel dake yankin Ikotun a jihar Lagos inda anan ne aka bata ganyen tabar wiwin domin tayi safarar ta.