NDLEA ta kama wata mata kan hanyarta ta zuwa Qatar da  ganyen tabar wiwi

Jami’an hukumar NDLEA dake yaÆ™i da hana sha da kuma fataucin miyagun Æ™wayoyi sun tsare wata mata Æ´ar shekara 35 mai suna, Chidimma Okene.

An tsare matar ne bayan da aka kama ta tana ƙoƙarin safarar ƙunshi 20 na ganyen tabar wiwi mai nauyin 10.70Kg da aka ɓoye cikin abincin ƙabilar Igbo da ake kira Abacha da kuma busassun kayan lambu lokacin da take hanyar zuwa garin Doha dake ƙasar Qatar ta filin jirgin Saman Murtala Muhammad dake Lagos.

Hukumar ta ce jami’anta da haÉ—in gwiwar jami’an hukumar DSS ne suka samu nasarar kama matar lokacin da ake tantance fasinjojin da suke shirin hawa jirgi.

Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi ya ce Chidimma tana zaune ne a ƙasar Qatar kuma ta dawo gida Najeriya domin yin bikin Kirsimeti.

Chidimma ta ce an ajiye ta ne a  Club Dice Hotel dake yankin Ikotun a jihar Lagos inda anan ne aka bata ganyen tabar wiwin domin tayi safarar ta.

More News

Ƴan sanda sun kama mutane 50 kan rikicin da ya faru a wata kasuwa a Lagos

Rundunar Æ´an sandan jihar Legas ta kama mutane sama da 50 da ake zargin suna da hannu rikicin da ya faru a kasuwar Ile...

Ƴan Sanda sun kama wanda ya shirya kai harin jirgin ƙasar Abuja-Kaduna a shekarar 2022

Rundunar ƴan sandan Najeriya ta ce jami'anta sun kama wani mutum mai suna Ibrahim Abdullahi wanda ake zargi da kitsa harin jirgin ƙasar da...

Sojoji Sun Ceto Mutane Daga Hannun Masu Garkuwa Da Mutane A Filato

Dakarun rundunar Operation Safe Haven dake aikin tabbatar da tsaro a jihar Filato da wani É“angare na jihar Kaduna sun samu nasarar ceto mutane...

Matatar Mai Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki A Ƙarshen 2024

Kamfanin Kaduna Refining and Petrochemical Company KPRC ya ce matatar mansa za ta fara aiki a shekarar 2024. Mustapha Sugungun managan matatar man ta KRPC...