NDLEA ta kama wata mata kan hanyarta ta zuwa Qatar da  ganyen tabar wiwi

Jami’an hukumar NDLEA dake yaÆ™i da hana sha da kuma fataucin miyagun Æ™wayoyi sun tsare wata mata Æ´ar shekara 35 mai suna, Chidimma Okene.

An tsare matar ne bayan da aka kama ta tana ƙoƙarin safarar ƙunshi 20 na ganyen tabar wiwi mai nauyin 10.70Kg da aka ɓoye cikin abincin ƙabilar Igbo da ake kira Abacha da kuma busassun kayan lambu lokacin da take hanyar zuwa garin Doha dake ƙasar Qatar ta filin jirgin Saman Murtala Muhammad dake Lagos.

Hukumar ta ce jami’anta da haÉ—in gwiwar jami’an hukumar DSS ne suka samu nasarar kama matar lokacin da ake tantance fasinjojin da suke shirin hawa jirgi.

Mai magana da yawun hukumar ta NDLEA, Femi Babafemi ya ce Chidimma tana zaune ne a ƙasar Qatar kuma ta dawo gida Najeriya domin yin bikin Kirsimeti.

Chidimma ta ce an ajiye ta ne a  Club Dice Hotel dake yankin Ikotun a jihar Lagos inda anan ne aka bata ganyen tabar wiwin domin tayi safarar ta.

More News

Zanga-zanga: An jibge Æ´an sanda 4200 a Abuja

Rundunar Æ´an sandan birnin tarayya Abuja ta tura Æ´an sanda 4200 gabanin zanga-zangar da za a gudanar a cikin watan Agusta. Kamar yadda masu shirya...

Kamfanin NNPC ya shirya daukar karin ma’aikata

Kamfanin mai na Nigerian National Petroleum Company Limited ya shirya daukar karin ma’aikata.Kakakin kamfanin na NNPC, Olufemi Soneye, ya tabbatar da hakan a wata...

Ya kamata matasa su yi haÆ™uri zanga-zanga ba ita ce mafita ba – Sarkin Zazzau

Sarkin Zazzau, Mai Martaba Ahmed Nuhu Bamalli ya ce matasa su ƙara haƙuri da gwamnatin tarayya su janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa a...

Zanga-zanga: Tinubu ya gana da gwamnonin APC

Shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu ya gana da gwamnonin da aka zaɓa ƙarƙashin jam'iyar APC. Taron ganawar da aka gudanar a fadar shugaban ƙasa ta...