Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, ta ayyana yajin aikin gargadi na kwanaki biyu a fadin kasar, wanda zai gudana a ranakun 5 da 6 ga watan Satumba, tare da wa’adin gwamnatin tarayya na magance matsalolin da talakawa ke fuskanta.
Shugaban kungiyar ta NLC, Joe Ajaero ne ya bayyana hakan a yayin wani taron manema labarai da ya gudanar a karshen taron majalisar zartarwa ta kasa ranar Juma’a a Abuja.
Ajaero, a lokacin da yake gabatar da sanarwar tare da sanya hannun Mista Emmanuel Ugboaja, babban sakataren majalisar, ya jaddada cewa, wannan hukuncin an yanke shi ne sakamakon tattaunawa mai zurfi a tsakanin shugabannin kungiyar.
Kungiyar ta NLC ta sanar da gwamnati, inda ta bayyana cewa idan ba a dauki mataki ba, za a iya tsayar da al’amura a kasa baki daya ba tare da wani lokaci ba a cikin kwanaki 14 zuwa 21 masu zuwa.
Babban makasudin wannan yajin aikin, in ji Ajaero, shine tursasa gwamnati ta magance munanan matsaloli da talauci da ake fuskanta a fadin kasar.