Yan bindiga sun harbe wani manomi tare da sace mutane 7 a Kaduna

Ƴan bindiga sun harbe wani manomi tare da sace karin wasu mutane 7 ;maza biyu mata biyar a kauyen Unguwar Gajere dake mazabar Kutemeshi a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.

An kai wa mutanen farmaki ne lokacin da suke aiki a gonakinsu a ranar 2 ga watan Agusta.

Mamba mai wakiltar mazabar, Kakangi a majalisar dokokin jihar, Yahaya Musa shi tabbatar da faruwar lamarin inda ya ce yan bindigar sun kuma sace dabbobi a kauyukan dake kusa da garin.

A cewar sa halin da ake ciki abun damuwa ne sosai inda ya jajantawa iyalan da suka yi asarar rayukan yan uwansu.

Ya ce yawanci yan bindigar suna satar shanu a kauyukan Gwandu da Damari.

Wan mazaunin kauyen ya ce kauyukan suna yawan fuskantar hare hare daga yan bindigar inda ya ce kisan na neman zama abin dake faruwa kullum. Ya yi kira da akawo musu dauki daga hukumomin da abin ya shafa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]