Gwamnatin Najeriya ta gurfanar da Emefiele saboda zargin mallakar makamai ba bisa ka’ida ba

Gwamnatin tarayya ta gurfanar da Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin Najeriya da aka dakatar,bisa tuhume-tuhume biyu da suka hada da mallakar makamai ba bisa ka’ida ba.

An gurfanar da shi ne a gaban babbar kotun tarayya.

A cewar rahoton gidan talabijin na Channels a ranar Lahadi, gwamnatin tarayya ta zargi Emefiele da mallakar bindiga ba tare da lasisi ba.

Gwamnati ta yi iƙirarin laifin ya ci karo da Sashe na 4 na Dokar Makamai.

Baya ga tuhumar, ana tuhumar Emefiele da mallakar harsashi har guda 123 ba tare da lasisi ba.

More from this stream

Recomended

Trump Ya Yaba Wa Tinubu Kan Yaƙi Da Ta’addanci A Najeriya

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yaba wa Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan abin da ya bayyana a matsayin ƙwazon jagorancinsa wajen yaƙi da ta’addanci da magance matsalar tsaro a ƙasar. A cewar Fadar Shugaban Ƙasa, Trump ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aike wa Tinubu. Ya ce yana yaba wa shugaban […]