Yan sanda A Abuja Sun Kama Wani Yaro Ɗan Shekara 16 Da Ya Kashe Mahaifinsa

Rundunar yan sandan birnin tarayya Abuja, ta ce jami’an ta sun kama wani yaro mai shekaru 16 da ake zargi da kashe mahaifinsa.

Kwamishinan yan sandan birnin tarayyar, Haruna Garba shi ne ya bayyana haka lokacin da yake ganawa da manema labarai.

Ya ce wanda ake zargi ya kashe mahaifinsa ne ta hanyar amfani da taɓarya.

A cewar kwamishinan lamarin ya faru ne lokacin da mahaifiyar wanda ake zargi da kuma mahaifinsa suka rikice da faɗa a a tsakaninsu inda Wanda ake zargin ya shigarwa mahaifiyarsa inda yayi amfani da taɓarya ya daki mahaifin nasa a kansa da karfi inda hakan ya yi sanadiyar mutuwarsa.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]