Kotu za ta yanke hukunci kan rikicin APC a Kano.

A yau Talata ne ake sa ran Kotun Ɗaukaka Ƙara za ta yi zaman sauraron ƙarar rikicin shugabanci a jam’iyyar APC mai mulkin Jihar Kano tsakanin Gwamna Abdullahi Ganduje da ɓangaren Sanata Ibrahim Shekarau.

Ɓangaren Gwamna Ganduje ne ya ɗaukaka ƙarar bayan ya sha kaye a shari’o’i biyu da suka gabata, inda yake neman a soke shugabancin Ahmadu Haruna Zago, wanda ke samun goyon bayan tsohon Gwamna Shekaru, sannan a bayyana Abdullahi Abbas a matsayin halastaccen shugaba.

A wata shari’ar ta kotun tarayya na baya, kotun ta bayyana cewa ɓangaren Ganduje ba shi da hurumin neman a kori ƙarar saboda ya riga ya ɗaukaka ƙara a Kotun Ɗaukaka Ƙara, saboda haka ne kuma ta yi watsi da buƙatarsu.

Rikicin APC a Kano ya samo asali ne tun bayan gudanar da tarukan jam’iyyar a matakin mazaɓu da jiha, abin da ya haddasa aiwatar da taruka biyu ƙarƙashin Sanata Ibrahim Shekarau da kuma ɓangaren gwamnatin Kano.

More from this stream

Recomended

Kotun Tarayya Ta Tabbatar Da David Mark A Matsayin Shugaban ADC

Wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta tabbatar da shugabancin jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ƙarƙashin jagorancin tsohon shugaban majalisar dattawa, David Mark. Kotun ta yi watsi da ƙarar da ɗan majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar kan shugabancin jam’iyyar, inda ta bayyana cewa lamarin ya shafi harkokin cikin gida na jam’iyyar siyasa. Mai […]