
“Ba wai ayuka ne suka yi wa Sheikh yawa ba. Matsalar ita ce gwamnati ba ta da sha’awar sulhuntawa ta wadannan mutanen. Saboda haka Sheikh ya yi kokarin bin wasu hanyoyi domin cimma burinsa,” in ji Salisu Hassan.
Ko baya ga ziyartar shugabanni, Sheikh Gumi ya yi tattaki zuwa wasu dazuka a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Naija, inda ya sadu da ‘yan bindigar da suka addabi yankin da hare-hare, kisan jama’a da satar mutane domin karbar kudin fansa.
Malamin yayi wa ‘yan bindigar wa’azi, tare da shawartar su da su ajiye makamai, su shigo gari domin gwamnati ta yi musu afuwa, su kuma su daina miyagun ayukan da suke yi.
To sai dai tuni matakin na Gumi ya hadu da kakkausan suka daga wasu shugabanni kamar gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai da ma shugaban kasa Muhammadu Buhari.
Haka kuma jawaban malamin akan abin da ya bayyana a matsayin “danne hakki da ‘yancin mutanen ne ya sa su daukar makamai suka shiga daji,” sun ja hankalin manazarta lamurran tsaro, masu ganin cewa kalaman malamin na da hatsarin gaske ga sha’anin tsaron kasa.
Gwamna Nasir El-Rufa’i na daga cikin shugabanni na farko da ya soma yin fatali da shawarar Gumi, inda ya sha alwashin cewa sam bai ga dalilin yin sulhu da ‘yan ta’adda ba.
Saurari kalaman Gwamna El-Rufa’i dangane da zancen yin sulhu da ‘yan bindiga.
Wasu rahotanni sun bayyana cewa bayan ziyarar dazukan, Sheikh Gumi ya yi kokarin ganawa da shugaban kasa Muhammadu Buhari, domin tattaunawa akan abin da ya gano daga ziyarar ta shi, da kuma yiwuwar shata tafarkin yin sulhu da afuwa ga ‘yan bindigar da ke da bukatar ajiye makamai.
To sai dai rahotannin sun ce bayan kwashe tsawon fiye da wata daya yana yunkurin, malamin bai sami nasarar ganin shugaban kasar ba, lamarin da kuma ya sanyaya masa gwiwar ci gaba da kokarin samar da sulhu da afuwa ga ‘yan bindigar.